Header Ads Widget

Yanzu-yanzu: An sake sassauta dokar kulle saboda zanga-zanga a Kano

Yanzu-yanzu: An sake sassauta dokar kulle saboda zanga-zanga a Kano



By Muhammad Salisu, Kano 

Gwamnatin Jihar Kano a karo na biyu ta sake sassauta dokar kulle data saka ta yadda a yanzu jama'a zasu dinga futa daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma.

Gabanin wannan lokacin dai gwamnatin ta fara sassauta dokar kullen data fara sanarwa ta awanni 24 sakamakon hatsaniyar data biyo bayan Zanga-zangar lumana a Kano, inda ta rage lokacin dokar daga 8 zuwa 2 na rana, bayan da a karo na biyu aka sake sassauta dokar bisa la'akari da fara samun komawar lamura yadda suke a sassan Jihar.

Kwamashi nan ya sanda na jihar, Salaman Dogo ne ya sanarda hakan ga manema labaru jim kadan bayan kammala taron Majalisar tsaro ta jiha da ya gudana a Talatar nan wanda Gwamna Abba Kabir Yusif ya jagotanta a gidan gwamnatin Kano.

Kwamashinan Yan sandan yace Majalisar tayi nazari sosai game da halinda ake ciki a fadin jihar biyo bayan yamutsin da ya faru a jihar lokacin fara zanga-zangar lumanar dake gudana a sassan Nigeria.

Yace, Gwamnati da hadakar Jami'an tsaro za su cigaba da bibiyar yanayin tsaro domin yin abinda ya kamata a kowanne lokaci domin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya da cigaban al'amuran yau da kullun a fadin jihar Kano.

Newskeeper ta rawaito cewa, taron Majalisar tsaron ta jiha wanda ya dauki tsahon sama da awanni biyu, ya samu halartar Shugabannin dukkanin hukumimin tsaro dake Jihar Kano.

Post a Comment

0 Comments