Header Ads Widget

Ana fargabar sace wasu Kananan Yara kusan 20 a Maradun ta jihar Zamfara | Newskeeper

Image: (Google)

By Aisha Saleh

Ana fargabar sace wasu Kananan Yara da yawan su ya kai kusan 20 a Maradun ta jihar Zamfara.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru da safiyar Lahadin nan, a lokacin da yaran suka je itacen girki a kusa da babban asibitin garin na Maradin.

Wani dan garin na Maradun da ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar wa da da manema labarai cewa, maharan sun je da muggan makamai a bisa babura a lokacin da suka sace yaran.

Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta hannun kakakinta, DSP Yazid Abubakar ta ce za ta bincika domin kara tabbatar da lamarin ga manema labarai.

Post a Comment

0 Comments