Header Ads Widget

Nijar da Burkina Faso da Mali za su kafa kamfanin sufurin jiragen sama | Newskeeper Hausa

Hoto: Shugabannin Kasashen Niger, Mali da Burkina Faso

By Aisha Saleh 

Ministan sufuri a Nijar, Kanal Manjo Salissou Mahaman Salissou ya ce Ĉ™awancen Ĉ™asashen Sahel, da ya haɗa Burkina Faso da Nijar da Mali, na shirin kafa kamfanin sufurin jirgin sama domin Ĉ™arfafa haɗin gwiwar sabuwar Ĉ™ungiyar, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta ActuNiger ta ruwaito.

Salissou ya ce kafa kamfanin sufurin jirgin saman na AES abu ne mai muhimmanci da za su mayar da hankali a kai, kuma nan ba da jimawa ba za su samar da kamfanin mai launin Ĉ™asashen, wanda zai haɗa manyan biranensu da ma wasu wuraren.

Ministan ya kuma ce shugabannin mulkin soji a Niamey sun umurci hukumomin da ke kula da fannin sufurin jiragen sama su 'sassauta wasu dokoki'' domin a gaggauta samar da kamfanin jirgin sama na yankin da ma na Ĉ™asar.

A baya Ĉ™asashen Ĉ™awancen na AES waɗanda ke Ĉ™arĈ™ashin mulkin soji sun Ĉ™addamar da fasfo ɗin bai-ɗaya, sun kuma sanar da kafa dakarun haɗin gwiwa domin daĈ™ile Ĉ™ungiyoyin Ĉ´an bindiga da ke addabar yankin bayan ficewar su daga Ĉ™ungiyar ECOWAS.

Post a Comment

0 Comments